olNGIb4NkK5r2x7x4oG3GpEzizVpnY6KNCck9cym

Tambuwal Da Saraki Sun Bayyana Aniyarsu Ta Takarar Shugabancin Nigeria!



Gwamnan ihar Sakkwato Aminu Waziri Tambuwal ya yanki tikitin neman tsaya wa takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar PDP a babban zaben badi.

Da yammacin ranar Alhamis ne gwamnan ya karbi fom din a ofishin jam'iyyar PDP a Abuja.

Tambuwal ne mutum na biyu da ya ayyana aniyyarsa ta yin takarar ranar Alhamis, bayan tun da farko Shugaban Majalisar Dattawan kasar Abubakar Bukola Saraki ya ce zai tsaya takarar.

A ranar Laraba ne tsohon gwamnan Kano Satanata Rabiu Musa Kwankwaso ya yi gangamin kaddamar da takararsa a Abuja.

Aminu Tambuwal dai yana yin wa'adinsa ne na farko a matsayin gwamnan jihar Sakkwato, wanda aka zabe shi a shekarar 2015.

Gwamnan na Sakkwato yana daga cikin manyan 'yan siyasar kasar da suka fice daga APC zuwa PDP a watan Yuli.

Wasu dai na ganin bukatar takarar shugabancin kasar ce ta fitar da shi daga APC, kasancewar ba zai yi samunta a jam'iyyar ba, bayan da Shugaba Buhari ya nuna aniyyarsa ta yin takara a karo na biyu.

To sai dai gwamnan ya ce ya bar jam'iyyar ne saboda gwamnatin Buhari ba ta yi wa jiharsa komai ba.

Akwai dai mutane da dama da suka nuna aniyyarsu ta tsayawa takara a jam'iyyar ta PDP, kuma hakan ta sa ake ganin za a fafata sosai a zaben fidda gwani na jam'iyyar.


Zan Tsaya Takarar Shugabancin Nigeria (Saraki)

Shugaban majalisar dattawan Najeriya, Bukola Saraki, ya bayyana aniyarsa ta son tsayawa takarar shugabancin Najeriya a zaben 2019 a karkashin jam'iyyar PDP.

Saraki ya yi wannan maganar a lokacin da yake ganawa da matasa masu son yin takara, a birnin Abuja ranar Alhamis.

Ya ce kasar tana fuskantar zabi tsakanin sauya yadda take ko kuma ta cigaba da kasancewa yadda ta ke da.

Kwanan nan ne dai shugaban majalisar dattawan Najeriyar ya sauya sheka daga jam'iyyar APC mai mulki ya kuma koma PDP bayan wasu 'yan majisalr dokokin kasar kimanin 50 sun sauya sheka.

Cikin 'yan majalisar dokokin Najeriyar da suka sauya sheka din daga APC zuwa PDP akwai Rabiu Musa Kwankwaso, wanda ya yi shelar aniyarsa ta takarar shugabancin kasar ranar Laraba.

Saraki ne na baya-bayannan da ya ayyana aniyar takarar shugabancin Nigeriya a karkashin jam'iyyar PDP.

Sauran sun hada da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, da tsohon gwamnan jihar Jigawa Sule Lamido, da tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau, da Sanata Ahmed Makarfi.

Akwai kuma gwamnan jihar Gombe Ibrahim Hasan Dankwambo, da tsohon minista Kabiru Tanimu Turaki, da Dr. Datti Baba Ahmed, da tsohon gwamnan Sakkwato Attahiru Bafarawa, da tsohon mataimakin gwamnan babban bankin Najeriya Kingsley Moghalu.


Related Posts

Related Posts

Post a Comment